A ci gaba da yi wa harshen Hausa da al’adunsa hidima an samar da makarantar Hausa ta farko a kasar Togo wadda hausawan kasar suka assasa karkashin kungiyar Hausawa ta Association Tarayya Togo da hadin gwiwar gamayyar kungiyon hausawa na kasashen Afrika mai suna Gidauniyar Zumunci.
31/7/2023 aka bude wannan makarantar Hausa ta farko a Kasar Togo da dalibai goma sha biyar 15 karkashin kulawa da koyarwar Malam Muhammad Rabiu Abu Hidaya,
Abu Hidaya shi ne, shugaban Tsangayar Adabin Hausa haka kuma mataimakin shugaban gamayyar kungiyoyin hadaka na harshen Hausa (GIZU) wanda shi ne malamin da ya taso daga Nijeriya zuwa kasar Togo don bayar da horo ga daliban da za su yi nazarin harshen Hausa a makarantar Hausa ta farko a Togo.
Hausawa a kasar Togo sun dade don sun shafe kimanin shekaru dari biyar(500) a cewar Shugaban Kungiyar Tarayya Togo mai suna Alhaji Sulaiman Yahaya(Bala) kuma hukumar kasar Togo ta sanya su cikin ‘yan asalin kasar, masu aiki a dukkan sassan madafun iko na gwamnati.
saboda nisan lokaci harshe da al’adun sun soma jin jiki, wannan ne dalilin da suka yunkura suka assasa wannan makaranta don ci gaban harshen Hausa a matakin ilimi.
Kamfanin Gidan Dabino International tare da hadin gwiwar Gidauniyar Bukar Usman sun tallafawa wannan sabuwar makaranta da gudummuwar littattafan nazarin Hausa da kuma na dakin karatu don masu nazari.
Ana fata wannan yunkuri zai ci gaba da samun tagomashi daga jami’o’i da masu ruwa da tsaki kan ci gaban harshen Hausa a duniya.
Taron dai ya samu halartar dattawa da manya jami’an gwamnatin kasar tare da wakilcin gungun sarakunan kasar Togo.







