Sakamakon rashin fitar da dabbobi ƙasashen waje dabbobi a kasar Nijar sun yi kwantai.
Kusan a kowacce shekara ma su siyar da dabbobin sun dogara ne da masu shigowa daga wasu ƙasashen don sayan dabba.
Amma a wannan shekara dabbobin sun yi yawa inda har wasu na mutuwa saboda babu masu siya, wanda hakan ya samo asali ne daga hukuncin da hukumar mulkin Soja ta ƙasar ta yi na hana fitar da dabbobin zuwa wasu ƙasashen ketare.
Duk da cewa hukumar kasar ta Nijar ta amincewa wasu motoci masu dauke da lambar sufuri na musamman jigilar dabbobin zuwa kasar Burkina Faso, amma ‘yan kasuwar dabbobin na kokawa game da rashin ciniki a wannan shekara.












